Shugaban ƙungiyar Emmanuel Asodeke ne ya sanar da tsawaita yajin aikin a wata sanarwa da ASUU ɗin ta fitar, wanda ya ce an ɗauki matakin ne bayan da Kwamitin Zartarwa ya yi wani taron gaggawa a sakatariyar ƙungiyar da ke Jami’ar Abuja.
Mista Asodeke ya ce bayan tattaunawa sosai da gwamnati kan kawo ƙarshen yajin aikin zuwa yanzu ta gano cewa gwamnati ta ƙi ɗaukar haƙƙoƙin da suka ratayu a wuyanta kan batutuwan da ƙungiyar ta bujiro da su a shekarar 2020.
“Hakan ne ya sa muka sake tsawaita yajin aikin da mako 12 domin bai wa gwamnati lokaci don warware matsalolin da suke a ƙasa,” in ji shi.